Karshen Duniya Kalli Yadda Wannan Daliban Macce Da Namiji Suke Aikata Lalata A Wajen Shakatawa Gaban Mutane

Karshen Duniya Kalli Yadda Wannan Daliban Macce Da Namiji Suke Aikata Lalata A Wajen Shakatawa Gaban Mutane


 WAI SUN WAYE

Ni kuma banga abin burgewa da wayewa anan ba, sai dai na ga zallan rashin kunya, rashin tarbiyya da rashin mafadi

Dabi’un yahudu da nasara irin wannan ko Musulmi ya koya baya masa kyau, karshensa nadama ne

Da hankalina da wayona da addinina na Musulunci ba zan iya aikata haka da kowace irin mace ba balle matar da zan aura, balle kuma na dauka a hoto na yada a duniya

Kwanaki na ji wani Malami yana cewa saurayi da budurwaa da suka tashi zasuyi aure suna kwashe albarkan auren tun a gurin daukar hoto kafin aure saboda abubuwa na wuce iyaka, haram da sabon Allah da suke aikatawa 

Ko ka biya sadaki tunda dai ba’ayi siga ba, kuma babu shaidu to baka da lasisin da zaka rungumeta, ko ka tsotsi bakinta a dalilin daukar hoto kafin aure, aikata hakan laifine babba, kuma yana kwashe albarkan aure

 

Allah Ka shiryar da su

LESBIAN!

 

Dear Sister 💕 

Ke musulma ce? Kuma kin yi imani wata rana zaki farka a kabari? Kinyi imani wata rana Mala’iku zasu tayar dake suyi Miki tambaya akan ayyukan ki?

 

Na san ke mace ce mai hankali, nutsuwa da kamala. Ki kula kuma ki zauna ki yi tunani wallahi wannan abu yana da illa kuma kazanta ce. Saboda kazantarta ce masu yi basu bari a sani. Ki kula da duniya kafin ta kai ki ta baro ki. Rayuwar duniya ƙalilance a kan na lahira. Allah ya yi miki ni’ima, ya baki lafiya,hankali,ya suturta ki, ya baki ƴanci da ya yi ki musulma, ta wanna hanyar zaki gode masa?

 

Shin labarin mutanen Lud bai iso gare ki ba?

Waɗanda aka juya kasar su aka kife su,sannan aka musu ruwan duwatsu, sannan aka bar hakan ya zama iznā ga mu da muka zo bayan su? Ko dai baki karanci tarihin su ba? Ko dai Qur’ani ba littafin Ubangijin ki bane? Ko dai kuma iƙrarin Musulunci ne a baka, amma zuciyar ki cike take da akasin haka?

 

Wallahi mutuwa tabbas ne, hisabi wajibi ne kuma wuta gaskiya ce. Ki tsare kan ki daga azaba mai tsanani da muni.

Tarbiyya tayi mummunar lalacewa a wannan zamanin tamu, kuma dole a tashi a gyara, a daina kunyar kiran waɗan nan zuwa ga dai-dai, ko kuwa a haka za su dinga jan kannen mu da ƴan uwan mu gare su, idan ba a nuna hakan mummunan aiki bane, to da sannu shaiɗan zai ƙawata shi ya zam mai kyau.

“Idan masu Ilimi basu karantar ba, da sannu wawaye da jahilai zasu yi tallar shashancin su”

Abin takaici yanzu wannan abin ya yawaita tsakanin matan hausawan mu har ta kai ta kawo yanzu wasu basu da wani buri face su kusanci ƴan uwan su mata,dalilin haka yanzu wasu matan gaba ɗaya sun cire ma kansu feeling a kan namiji sai dai su ji sha’awar ƴan uwan su mata🤦‍♂️

Kuma ko baku so zamu faɗa: Yadda Ƴan mata yanxu suke da ƙawayen su ne duk yake janyo irin wannan, zaka ga suna rungumar junan su,suna sumbatar su,har suke ƙebewa suna ganin Private part na Junan su, duk da sunan wayewa bayan kin san addinin ki ya haramta haka kuma ba haka kika taso kika ga iyayen ki suna yi ba

Post a Comment

0 Comments